[1] Tirmidhi juzu'i na 2 cikin "Manakib Ahlulbaiti" shafi na 308 daga Umar ibn Abi Salama, wanda ya ce: an saukar da ayar "…Allah na nufin Ya tafiyar da kazamta kawai daga gare ku, Ya ku mutanen babban gida, kuma ya tsarkakeku tsarkakewa" a gidan Ummu Salma. Daga nan sai Manzon Allah (s.a.w.a.) ya kira Fadima, Hasan, Husaini da Ali ya rufe su da mayafi, ya ce: "Ya Allah! Wadannan su ne Ahlulbaiti, don haka Ka tafiyar da kazamta daga gare su Ka tsarkake su tsarkakewa". Sai Ummu Salma ta ce: "Ya Manzon Allah shin ni ma ina daga cikinsu ne?, sai ya ce mata: "Ke dai kina a matsayinki, ke kina a kan alheri".

[2] An ruwaito wannan hadisi cikin littafin Ghayat al-Maram daga Abdullah ibn Ahmad ibn Hambal ta hanyoyi uku daga Ummu Salama, haka nan ma cikin Tafsirin Tha'alabi…haka nan ma Ibn Mardawihi da Khadib daga Abi Sa'id Khudri da wannan ma'ana sai dai kawai 'yan canje-canje na lafazi. Haka nan kuma an ruwaito shi cikin Ghayat al-Maram daga Abdullahi bn Ahmad bn Hambal daga babansa da isinadinsa zuwa ga Ummu Salama, dubi Al-Mizan fi Tafsiril Kur'an na Allama Tabataba'i kan Ayar Tsarkakewa. Wanda kuma ya ke son karin bayani kan wasu masdarori na musamman kan tafsirin wannan aya da kuma gabatarwa kan Ahlulbaiti guda biyar (a.s.) to sai ya karin bayani da ke karshen wannan littafi.

[3] Ibn Jarir da Ibn Abi Hatam da Dabarani sun ruwaito wannan hadisi daga Abi Sa'id Khudri, kamar yadda kuma aka ruwaito shi cikin Ghayat al-Maram da Tha'alabi cikin tafsirinsa, a cikinsa Tirmidhi ya ruwaito shi kuma ya ingantar da shi, da kuma Ibn Jarir da Ibn Munzir da Hakim, kuma duk sun ingantar da shi. Haka nan ma Ibn Mardawihi da Baihaki cikin Sunan dinsa ta hanyar Ummu Salma. Dubi Al-Mizan fi Tafsiril Kur'an na Allama Tabataba'i.

[4] Buhari da Muslim duk sun ruwaito ta hanyar A'isha/ Ghayat al-Maram, haka nan kuma Zamakhshari ya ambato shi cikin tafsirin al-Kashshaf ya yin da yake tafsirin Ayar Mubahala.

[5] Ibn Mardawihi daga ibn Abi Shaibah da Ahmad da kuma Tirmidhi sun ruwaito kuma sun inganta shi, sannan kuma Ibn Jarir da Ibn Munzir da Dabarani da Hakim, kuma sun inganta shi, da kuma ibn Mardawihi daga Anas. Mai son karin bayani sai ya duba Al- Mizan na Tabataba'i yayin da yake magana a kanAyar Tsarkakewa.

[6] Jami al Usul, juzu'i na 9, shafi na 156 ya nakalto daga Sahih Tirmidhi, haka nan ma Hakim ya ruwaito shi cikin Mustadrak juzu'i na 3 shafi na 158, kuma ya inganta shi.

[7] Fadhl Aalulbaiti na Takiyuddin Ahmad bn Aliyu al Makrizi (wanda ya rasu a shekara ta 845 bayan hijira), shafi na 21.

[8] Fakhrurrazi cikin Tafsirul Kabir yayin tafsirin Surar Shura aya ta 23.

[9] Ghayat Maram yayin tafsirin ayar.

[10] Sanannen al'amari ga mai karatu cewa wannan fassara ta yi nisa ga hakikanin ma'anar kalmar, don kuwa ma'anar kalmar aal a cikin harshen Larabci a fili yake, babu yadda za a fassara kalmar aal da al'umma.

[11] Rafdhu a wajen malaman Ahlussunna shi ne yarda da cewa Imam Ali bn Abi Talib (a.s.) shi ne halifan Manzon Allah (s.a.w.a.) na farko bayan rasuwarsa. Kuma Rafidhi shi ne wanda ya yarda da hakan.

[12] Fakhrurrazi cikin Tafsirul Kabir, yayin tafsirin Surar Shura aya ta 23.

[13] Ihya'ul Mait bi fadha'il Ahlilbaiti na Suyudi shafi na 8, kuma Suyudin ya ruwaito shi cikin Durrul Mansur , juzu'i na 6 shafi na 7 ta hanyar Sa'id bn Jubair daga Ibn Abbas, sannan kuma Dabarani ma ya fitar da shi cikin Mu'ujamul Kabir, juzu'i na 1 shafi na 125. Haka ma Tabari ya ruwaito shi cikin Zakha'ir shafi na 25, yana cewa: "Ahmad ya fitar da shi cikin Munakib. Kamar yadda kuma Ibn Sabbag al-Maliki ya ruwaito shi daga Nabawiy daga Ibn Abbas, shafi na 29. Hakan nan kuma Kurdabi ya fitar da shi cikinsa Jami' al-Ahkam al-Kur'an da ruwayar Sa'id bn Jubair daga Ibn Abbas, juzu'i na 16, shafi na 21-22.

[14] Tabataba'i daga Sheik Tusi.

[15] Wannan tawaga ta kumshi manya-manyan shuwagabannin kiristocin Larabawa kamar haka: Abdul Masih, wanda ya kasance shugabansu, da kuma al-Ayhma, wanda ya kasance mai kula da al'amurran gudanarwa da ayyukan ibada, da kuma Abu Hatam ibn Alkama, wanda ya kasance bishof ne kana kuma kula da makarantunsu. Dubi Fusul al-Muhimma na Ibn Sabbag al-Maliki a sashin gabatarwar marubuci.

[16] Yin 'yar kuretsakanin vangare biyu kan Allah Ya saukar da azaba a kan vangaren da ba ya kan gaskiya. A takaice dai yin la'ananneniya tsakanin vangarori biyu don gano wani vangare ne ya ke kan gaskiya.

[17] Ashabul Kisa' (ma'abuta mayafi), suna ne da ake kiran mutanen da suka kasance tare da Manzon Allah (s.a.w.a.) cikin mayafinsa inda daga baya aka saukar da Ayar Tsarkakewa a gare su. Su ne kuwa: Aliyu, Fadima, Hasan da Husaini (a.s.), kamar yadda aka ambata a baya.

[18] Tafsirul Kashshaf na Zamakhshari yayin tafsirin Surar Ali Imrana aya ta 61, haka nan kuma ya zo cikin Tafsirin Tha'alabi daga Mujahid da Kalbi.

[19] Tafsirul Kabir na Fakhrurrazi a kanAyar Mubahala.

[20] Jumlar "....ku yi salati a gare shi.." wacce ta zo cikin ayar tana nuni da wajibci ne, don malaman Usul al-Fikh sun bayyana fi'ilin umurni a matsayin yana nuni ga wajibci ne, wasu ma suna ganin cewa a duk lokacin da fi'ilin umurni ya zo cikin Alkur'ani ko hadisi yana nuni ga wajibci ne sai dai idan akwai wani abin da yake nuni da cewa wajibcin ya koma zuwa ga mustahabi.

[21] Tafsirul Kabir na Fakhrurrazi a tafsirin Surar Ahzab aya ta 56.

[22] Almizan fi Tafsiril Kur'an na Allamah Tabataba'i, juzu'i na 16, shafi na 344.

[23] Allamah Hilli wanda ya kasance daga cikin manyan malaman fikihun mazhabar Ahlulbaiti (a.s), kuma yana daga cikin sanannun karni na bakwai bayan hijira, yayin da yake ambaton wajiban salla yana cewa: (Na bakwai) tahiya, wajaba ce a dukkan salla mai raka'o'i biyu sau guda, sannan kuma sau biyu a salloli masu raka'o'i uku da hudu, da mutum zai bar ta da gangan, to salla ta vaci. Akwai abubuwa guda biyar a cikin ko wane daya daga cikinsu da suka kasance wajibai, su ne kuwa: zama gwargwadon tahiya, yin shahadojin nan guda biyu da salati ga Annabi da Alayensa (a.s.). Dubi Shara'ii Islam, juzu'i na 1, babin salla.

[24] Zamakhshari cikin littafin al-Kashshaf, yayin tafsirin Surar Insan, haka nan kuma Fakhrurrazi shi ma ya kawo wannan ruwaya cikin littafinsa na Tafsir al-Kabir . Haka ma Tabrisi cikin Majma'ul Bayan.

[25] Birnin Makka ya fuskanci fari mai tsananin gaske kafin aiko Ma'aiki (s.a.w.a.), don haka sai Manzon Allah (s.a.w.a.) ya dauko Imam Ali (a.s.) daga wajen mahaifinsa Abu Talib (a.s.) zuwa gidansa don yi masa tarbiyya da kuma saukaka wa Baffansa (Abu Talib) wanda ya kasance fakiri ne.

[26] Zamakshari cikin al-Kashshaf yayin tafsirin Surar Ma'ida aya ta 55.

[27] Al-Wahidi cikin Asbabun Nuzul / Surar Ma'ida aya ta 55.

[28] Mai son karin bayani sai ya koma ga.....

[29] Hakim al-Haskani cikin littafin Shawahid al-Tanzil juzu'i na 1 shafi na 190 ya ruwaito cewa:
"Daga Abdulla bn Abi Aufa, yana cewa: Na ji Manzon Allah (s.a.w.a.) ya karanto wannan aya (sai ya karanto ayar Tabligh) a Ranar Ghadir Khum, sai ya daga hannayensa har ana ganin farin hammatansa, ya ce: "Ku sani duk wanda ya zamanto shugabansa, to Aliyu shugabansa ne".
Haka nan ma Al-Wahidi cikin Asbabun Nuzul shafi na 135, da kuma Suyudi cikin Durrul Mansur juzu'i na 2 shafi na 198, daga Abi Sa'id al-Khudri cewa: Wannan aya ta sauka ne dangane da sha'anin Aliyu bn Abi Talib.

[30] Majma' al-Zawa'id, juzu'i na 9, shafi na 163-165.

[31] Hakim al-Haskani ya ruwaito shi cikin juzu'i na 1, shafi na 192-193.

[32] Majma' al-Zawa'id, juzu'i na 9 shafi na 163-165, da kuma Ibn Kathir juzu'i na 5 shafi na 209-213.

[33] Tarikh ibn Kathir, juzu'i na 5 shafi na 213.

[34] Majma' al-Zawa'id.

[35] Musnad Ahmad juzu'i na 4 shafi na 281, Sunan ibn Maja babin falalar Ali, ta Tarikh ibn Kathir, juzu'i na 5, shafi na 209 da 210.

[36] Musnad Ahmad, juzu'i na 4, shafi na 281, Sunan Ibn Majah, babin falalar Ali, da kuma ibn Kathir, juzu'i na 5, shafi na 212.

[37] Basra sunan wata alkarya ce da ke kusa da Damaskus, San'a' kuma tana kusa da garin Bagadaza.

[38] Majma' al-Zawa'id da wasu kalmominsa daga ruwayar Hakim, juzu'i na 3, shafi na 109-110, da kuma Ibn Kathir, juzu'i na 5, shafi na 209.

[39] Musnad Ahmad, juzu'i na 1, shafi na 118 da 119, da kuma juzu'i na 4 shafi na 281, da Sunan Ibn Majah, juzu'i na1, shafi na 372, da Ibn Kathir, juzu'i na 5 shafi na 209.

[40] A cikin ruwayar Hakim al-Haskani, juzu'i na 1 shafi na 190, cewa ya yi: sai ya daga hannunsa har aka ga farin hammatarsa, sannan a cikin shafi na 93 kuma cewa ya yi: har farin hammatarsa ya fito.

[41] Hakim al-Haskani cikin Shawahid al-Tanzil, juzu'i na 1, shafi na 191, da kuma wurin Ibn Kathir, juzu'i na 5, shafi na 209 cewa ya yi: ni kuma ni ne majivincin kowane mumini.

[42] Musnad Ahmad juzu'i na 1 shafi na 118 da 119 da juzu'i na 4 shafi na 281 da 370 da 372 da 373 da juzu'i na 5 shafi na 347 da 370, da al-Mustadrak na Hakim, juzu'i na 3, shafi na 109, Sunan Ibn Majah da Hakim al-Haskani, juzu'i na 1 shafi na 190 da 191, da Tarikh ibn Kathir, juzu'i na 5 shafi na 209 da 210-213, inda ibn Kathir cikin juzu'i na 5 shafi na 209 ya ce: nace wa Zaid, shin ka ji hakan daga Manzon Allah (s.a.w.a.)? sai yace: Babu wani wanda yake gurin face ya gan shi ko kuma ya ji da kunnuwansa, sai Ibn Kathir ya ce: Malaminmu Abu Abdullah al-Zahabi ya ce: wannan hadisi ingantacce ne.

[43] Musnad Ahmad, juzu'i na 1 shafi na 118 da 119, Majma' al-Zawa'id juzu'i na 9 shafi na 104 da 105 da 107, da Shawahid al-Tanzil juzu'i na 1 shafi na 193, da Tarikh Ibn Kathir juzu'i na 5 shafi na 210 da 211.

[44] Shawahid al-Tanzil juzu'i na 1 shafi na 191, da Tarikh Ibn Kathir juzu'i na 5 shafi na 210.

[45] Shawahid al-Tanzil, juzu'i na 1 shafi na 190.

[46] Hakim al-Haskani ya ruwaito shi daga Abu Sa'id al-Khudri, juzu'i na 1 shafi na 157-158, hadisi 211-212, daga Abu Huraira shafi na 158 hadisi na 212, da kuma cikin Tarikh na Ibn Kathir juzu'i na 5 shafi na 214.

[47] Al-Mustadrak, juzu'i na 3, shafi na 129, Kanzul Ummal, juzu'i na 6, shafi na 157, Dabari ma ya ambaci haka cikin tafsirinsa da Fakhrurrazi cikin tafsirinsa na Al-Kabir, da kuma Suyudi cikin Durrul Mansur yayin da yake tafsirin wannan aya.

[48] Ibn jarir Tabari ya ambaci hakan, da kuma Suyudi cikin Durrul Mansur , da Zamakhshari cikin Al-Kashshaf yayin da yake tafsirin ayar, da kuma Wahidi cikin Asbabun Nuzul shafi na 200, da kuma Tarikh Bagdad da kuma Riyadhun Nadhrah.

[49] Suyudi cikin Durrul Mansur, Fakhrurrazi cikin tafsirinsa yayin tafsririn wannan aya, kamar yadda Al-Muntaki Al-Hindi cikin Kanzul Ummal juzu'i na 1 shafi na 251.

[50] Suyudi cikin Durrul Mansur karkashin tafsirin wannan aya, Kanzul Ummal juzu'i na 1 shafi na 237, Askalani cikin Fathul Bari juzu'i na 13 shafi na 27 da kuma Haithami cikin Majma'a juzu'i na 9 shafi na 194.

[51] Ibn Jarir Dabari ya ruwaito shi cikin tafsirin ayar, da kuma Zamakhshari cikin Al-Kashshaf yayin tafsirin ayar, Suyudi cikin Durrul Mansur yayin tafsirin ayar, haka nan ma Kanzul Ummal juzu'i na 6 shafi na 408, da kuma Wahidi cikin Asbabun Nuzul.

[52] Zamakhshari cikin tafsirin Al-Kashshaf, Suyudi cikin Durrul Mansur yayin tafsirin ayar, Riyadhun Nadhrah juzu'i na 2, shafi na 207 da kuma Ibn Hajar cikin Al-Sawa'ik al-Muhrika shafi na 102.

[53] Ibn Jarir Dabari cikin tafsirinsa, Suyudi cikin Durrul Mansur ta vangarori daban-daban, ya kara da cewa, a duk lokacin da Aliyu (a.s.) ya nufo wajen sahabban Manzon Allah (s.a.w.a.) sukan ce: Ga mafifitan alherin halitta (Khairul Bariya) ya iso. Haka ma an ruwaito wanda hadisi cikin Sawa'ikul Muhrika shafi na 96 da kuma cikin Nurul Absar na Shabalanji, shafi na 70 da kuma na 101.